IGP ya nada sabuwar mai magana da yawun rundunar 'yan sandan FCT

IGP ya nada sabuwar mai magana da yawun rundunar 'yan sandan FCT

  • Sifeta janar na ‘yan sanda, Usman Baba, ya amince da nadin DSP Josephine Adeh a matsayin jami’ar hulda da jama’an rundunar ta Abuja
  • Ya bayyana hakan a wata takarda ta ranar Talata a Abuja inda yace za ta fara aiki ne take yanke kuma ta maye gurbin ASP Daniel Ndirpaya
  • Dama kamar yadda rahotanni suka tabbatar, kafin a nada ta a wannan matsayin, Adeh ce ta biyu a harkar sadarwa ta musamman bangaren hulda da jama’a

FCT, Abuja - Sifeta janar na ‘yan sanda, Usman Baba ya amince da nadin DSP Josephine Adeh a matsayin jami’ar hulda da jama’an rundunar ‘yan sanda na babban birnin tarayya, Abuja.

Daily Nigerian ta ruwaito cewa, a wata takarda wacce ya saki a ranar Talata a Abuja, ya ce sabuwar jami’ar hulda da jama’ar za ta fara aiki ne take-yanke.

Kara karanta wannan

MIST: Gwamnatin Buhari ta amince wa sabuwar Jami’ar da aka kafa a Katsina ta fara aiki

IGP ya nada sabuwar mai magana da yawun rundunar 'yan sandan FCT
IGP ya nada sabuwar mai magana da yawun rundunar 'yan sandan FCT. Hoto daga dailynigerian.com
Asali: UGC

Adeh ta maye gurbin ASP Daniel Ndirpaya ne wanda yanzu aka yi wa karin girma zuwa kwamishinan ‘yan sanda na Abuja a ranar 31 ga watan Augusta.

Kamar yadda takardar ta bayyana, a da Adeh ce ta biyu a harkokin sadarwa na bangaren hulda da jama’a kafin a yi mata wannan nadin.

An ce sabuwar PPRO ta taba rike mukamin mataimakiyar mai bayar da shawarar ‘yan sanda na Police Attache a New York a Amurka.

“Adeh daya ce daga cikin mambobin Nigerian Institute of Public Relations sannan memba ce ta International Association of Chiefs of Police.
“Ta yi karatun Advanced Detective Course a Police Staff College da ke Jos,” kamar yadda takardar ta bayyana.

Sannan takardar ta ce za a iya samun sabuwar PPRO din ta lambar waya 07038979348 ko kuma Public Complaint Bureau a 09022222352 ko kuma adireshin yanar gizo na fctpolice@gmail.com

Kara karanta wannan

Hotunan ‘Pre-wedding’ din Jaruma Adamar Kamaye da wani Matashi suna yawo

Bayan 'yan fashin daji sun raba wasika, an tura karin 'yan sanda Sokoto

A wani labari na daban, rundunar 'yan sandan jihar Sokoto ta tura jami'ai yankunan da ake zargin miyagun 'yan fashin daji za su kai farmaki a jihar.

Premium Times ta ruwaito yadda wasu 'yan bindiga a makon da ya gabata suka raba wasika a harshen hausa inda suka sanar da yankunan shirinsu na kai musu farmaki.

A wasikar, 'yan bindigan sun sanar da mazauna yankin cewa, za su iya gayyatar sojoji sama da dari domin ba su kariya amma sai sun kai farmakin.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel