Shugaban NECO ya bayyana jihohin da ake mumunar satar Amsar jarabawa, Kano, Bauchi ke kan gaba

Shugaban NECO ya bayyana jihohin da ake mumunar satar Amsar jarabawa, Kano, Bauchi ke kan gaba

  • Jihar Kano, Bauchi da Bauchi sun fito zakaru cikin jihohin da ake mugun magudin jarabawa
  • Daliban sakandare na zana jarabawar NECO kowace shekara don kammala karatunsu
  • Shugaban NECO ya gabatar da jawabi kan yadda za'a magance matsalar satan jarabawa

Abuja - An bayyana jihar Bauchi, Kano da Kebbi a matsayin jihohin da ake mumunar magudin jarabawar kammala karatun Sakandare a Najeriya.

Shugaban hukumar Jarabawar kasa, NECO, Dantani Wushishi, ya bayyana haka, rahoton Punch.

Wushishi ya bayyana hakan ne a jawabin da ya gabatar a taron shugabannin makarantun dakehada karatun Boko da na Islamiyya mai take, 'Illar magudin zabe: Magance matsalar don cigaban kasa.'.

Ya kara da cewa magudi da satar amsa a jarabawa sun yi muni a Arewacin Najeriya amma abin ya fi muni a jihohin Bauchi, Borno, Kano da Kebbi a shekaru 5 da suka gabata.

Kara karanta wannan

Rikicin VAT: Jerin jihohi 10 da sukafi kowa samun kudin shiga da kuma 5 na kasan-kasa

Shugaban NECO ya bayyana jihohin da ake mumunar satar Amsar jarabawa
Shugaban NECO ya bayyana jihohin da ake mumunar satar Amsar jarabawa, Kano, Bauchi ke kan gaba Hoto: Getty Images

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

A cewar Wushishi,

"A 2016, alkaluman magudin jarabawa sun nuna Bauchi na 8.17%, Kaduna 6.20%, Kano 5.51%, Plateau 5.31%, da Sokoto 8.87%.
"A 2017, Bauchi (10.79%), Kebbi (16.06%), Borno (7.87%) da Kano (7.29%)."
"A 2018, Kano (12.45%), Kebbi (10.71%), Gombe (5.40%) da Zamfara (5.14%)."
"A 2019, Bornu (13.08%), Kano (11.70%), Kebbi (8.67%), Taraba (5.04%) and Yobe (6.56%)"
"Hakazalika a 2020, Adamawa (18.51%), Bauchi (7.88%), Kaduna (6.87%), Kano (7.88%) da Katsina (18.01%)."

Wushishi ya ce a shekaru biyar da suka gabata, Bauchi, Borno, Kano da Kebbi akafi samin satar jarabawa a Najeriya.

Nasarawa Poly ta sallami dalibai 51 kan laifin satar amsa a Jarabawa

A wani labarin, hukumar makarantar fasaha ta jihar Nasarawa watau Naspoly ta fittitiki dalibar 51 kan laifin satar amsa a jarabawar da aka gudanar a kakar karatun 2019/2020.

Kara karanta wannan

Jerin jami'o'i 10 da dalibai suka fi nema a Najeriya, Hukumar JAMB

Mai magana da yawun makarantar, Uba Maina, ya sanar da hakan a jawabin da ya saki ranar Laraba, rahoton NAN.

Mana yace kwamitin ingancin ilimi na makarantar ta amince da a sallami daliban.

Ya lissafa daliban tsangaya-tsangaya da aka sallama, daga cikinsu har da dalibai aikin jarida.

Asali: Legit.ng

Online view pixel