Rikicin VAT: Jerin jihohi 10 da sukafi kowa samun kudin shiga da kuma 5 na kasan-kasa

Rikicin VAT: Jerin jihohi 10 da sukafi kowa samun kudin shiga da kuma 5 na kasan-kasa

A ranar Juma'a, 16 ga watan Afrilu, hukumar lissafe-lissafen Najeriya (NBS) ta saki adadin kudin shiga jihohin Najeriya 36 da birnin tarayya suka samu a rubu'in karshe na shekarar 2020 da kuma na shekarar gaba daya.

Rahoton ya nuna cewa jihohin Najeriya gaba daya da FCT Abuja sun samu jimillan kudin shiga N1.31 trillion a 2020.

Legit ta lura cewa kudin da aka samu a 2020 yayi da kasa da abinda aka samu 2019 da N1.33 trillion.

Hakan na nuna cewa an samu nuksanin -1.93% (2019/2020)

Masana tattalin arziki sun bayyana cewa wannan ya faru ne sakamakon bullar cutar Korona a 2020.

A cewar rahoton, jihar Legas ce ta sama wajen samun kudin shiga N418.99 billion, sannan kuma jihar Ribas da ta samu N117.19 billion.

Kara karanta wannan

Naira ta yi kifewar da ba ta taba yi ba a tsawon shekaru 48, Dala $1 ta kai N550 a kasuwa

Ga jerin jihohi 10 dake sama wajen kudin shiga:

1. Lagos - N418.99 billion

2. Rivers - N117.19 billion

3. FCT - N92.05 billion

4. Delta - N59.73 billion

5. Kaduna - N50.76 billion

6. Ogun - N50.74 billion

7. Oyo - N38.04 billion

8. Kano - N31.81 billion

9. Akwa Ibom - N30.69 billion

10. Anambra - N28.00 billion

Jerin jihohi biyar na kasa

1. Jigawa - N8.66 billion

2. Gombe - N8.53 billion

3. Adamawa - N8.32 billion

4. Taraba - N8.11 billion

5. Yobe - N7.77 billion

Rikicin VAT: Jerin jihohi 10 da sukafi kowa samun kudin shiga da kuma 5 na kasan-kasa
Rikicin VAT: Jerin jihohi 10 da sukafi kowa samun kudin shiga da kuma 5 na kasan-kasa
Asali: Twitter

Dokar VAT za ta iya talauta Jihohi 30, Gwamna Wike yace sai dai sama da kasa su hade

Kara karanta wannan

Jerin jami'o'i 10 da dalibai suka fi nema a Najeriya, Hukumar JAMB

Jihohi da-dama a Najeriya ba za su iya sauke nauyin da ke kansu ba domin gwamnatin tarayya za ta rasa kaso na abin da take samu daga haraji daga wajen gwamnatin tarayya ba.

Mafi yawan jihohi sun dogara ne da kason da suke samu daga asusun hadaka na FAAC saboda gwamnoninsu ba su samun kudin-shiga.

Jihohin Ribas da Legas ne suke tattara 70% na harajin kayan masarufi a Najeriya, amma a karshe ana raba kudin ne tare da sauran gwamnonin jihohi 36

Gwamnan Ribas, Nyesom Wike da ya shigar da kara a kotu ya dage a kan bakararsa, yace ko sama da kasa za su hade ba zai bar FIRS ta karbi harajinsu ba.

Binciken da jaridar DailyTrust ta wallafa ya nuna cewa a halin yanzu jihohi 30 ba za su iya rike kansu ba idan abin da gwamnati take samu daga harajin VAT ya yi kasa.

Kara karanta wannan

Jerin kamfanoni 14 mallakin gwamnati da shugaba Buhari zai sayar saboda dalilai

Kotun daukaka kara ta hana jihar Legas da Rivers karbar kudin harajin VAT

Kotun daukaka kara dake Abuja ta dakatad da gwamnatocin jihar Rivers da Legas daga karbar kudin harajin VAT da hukumar FIRS ta saba karba daga hannun kamfanoni.

A hukuncin da Alkali Haruna Simon Tsanami ya yanke ranar Juma'a, ya bada umurnin cewa ayi watsi da sabuwar dokar da majalisar wakilan jihar Rivers ta kafa kuma gwamnan Wike ya rattafa hannu, rahoton DailyTrust.

Hakazalika majalisar dokokin Legas ta samar da irin wannan doka kuma gwamnan nan Babajide Sanwoolu ya rattafa hannu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel