Jerin Manyan Jihohi 10 da Suka Fi Yawan Kwararrun Likitoci a Najeriya, Rahoto

Jerin Manyan Jihohi 10 da Suka Fi Yawan Kwararrun Likitoci a Najeriya, Rahoto

Kwanan baya, kafofin yada labarai sun ruwaito ministan kwadago da aikin yi, Chris Ngige yana cewa Najeriya, Najeriya a matsayinta na kasa mai tasowa, da wuya ta cika ka'idar Majalisar Duniya da kuma kimar Hukumar Lafiya ta Duniya na samar da likita daya ga marasa lafiya 600.

A bangare guda kuma, ministan ya dage kan cewa Najeriya na da isassun likitocin da za su kula da mutane, yana mai cewa matsalar likitocin ita ce ba a turawa da rarraba ma'aikatan kiwon lafiya daidai gwargwado a wuraren da suka dace.

Ya ce yawancin likitocin kasar nan basu son aiki a yankunan karkara, sun zabi yin aikinsu a birane irinsu Abuja, Legas da Fatakwal.

Baya ga kwararrun likitocin cikin gida, Ngige ya ce likitocin da aka horar daga kasashen waje suma suna dawowa Najeriya don yin aiki.

Kara karanta wannan

Innalillahi: 'Yan Ta'adda Sun Kashe Basarake Bisa Kuskure, Sun Sace Mutum 3 a Wata Jihar Arewa

Rahoto: Jerin manyan jihohi 10 da suka fi yawan kwararrun likitoci a Najeriya
Likitocin Najeriya | Hoto: guardian.ng
Asali: UGC

Ministan ya yi ikirarin cewa a yanzu Najeriya tana da likitoci "kusan 4000 da 'yan kai”, inda ya dage cewa rashin kwararrun likitoci na da nasaba da rashin daidaita aikin.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Yace:

“Don haka, kusan kowa ya tafi Abuja, Legas da Fatakwal don zama. Kuma muna da cibiyoyin kula da lafiya na farko 10,000 wadanda aka yi watsu da su kamar yadda aka yi a kidaya ta karshe.”

Abin da alkaluma suka ce

A watan Agustan 2021, Ofishin Kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar da rahoton kididdigar shekarar 2020 kan mata da maza a Najeriya.

Daya daga cikin muhimman kididdiga da aka dauka a cikin rahoton shine adadin likitoci a kowace jaha na tarayya (gami da yawan mata daga cikinsu).

Bayanan da Legit.ng ta samu, sun samo asali ne daga Majalisar Likitocin Hakori ta Najeriya.

Kara karanta wannan

Karya suka min: Mai digiri ya fashe da kuka, ya kama kiwon kifi bayan kammala karatu

Manyan jihohi 10 mafiya yawan manyan likitoci (alkaluman 2019)

  1. Lagos - 2561
  2. FCT - 2523
  3. Ribas - 917
  4. Oyo - 772
  5. Edo - 727
  6. Kaduna - 711
  7. Kano - 632
  8. Delta - 554
  9. Anambra - 552
  10. Filato - 538

Sauran jihohin Najeriya

  1. Osun - 536
  2. Enugu - 491
  3. Ogun - 478
  4. Kwara - 446
  5. Borno - 377
  6. Bayelsa - 359
  7. Benue - 332
  8. Cross Riba - 330
  9. Imo - 319
  10. Ondo - 293
  11. Abiya - 289
  12. Gombe - 286
  13. Akwa Ibom - 278
  14. Katsina - 266
  15. Ekiti - 261
  16. Nasarawa - 258
  17. Bauchi - 243
  18. Kogi - 218
  19. Neja - 217
  20. Sokoto - 201
  21. Ebonyi - 184
  22. Adamawa - 147
  23. Kebbi - 144
  24. Zamfara - 137
  25. Yobe - 133
  26. Jigawa - 131
  27. Taraba - 86

Rahoton ya ci gaba da nuna cewa, tun daga shekarar 2019, Najeriya tana da likitoci 6,713 da ba a tantance su a karkashin kowace jiha ba. Adadin likitocin a kasar ya kai 24,640.

Kara karanta wannan

“Ta Tsere”: Matar Aure Ta Yashe Gaba Daya Asusun Bankin Da Suke Tara Kudi Da Mijinta, Ta Yi Batan Dabo

Sai dai, wani rahoto na baya-bayan nan da aka baiwa Hukumar Kula da Lafiya ta Najeriya ya bayyana cewa kusan likitoci 35,000 ne ke aikin a Najeriya.

Rahoton ya ci gaba da bayyana cewa, likitocin da ke aiki 35,000 suna cikin jimillar likitoci 80,000 da suka yi rajista da Hukumar Kula da Likitoci ta Najeriya (MDCN).

Wasu da ba sa aiki a Najeriya ana kyautata zaton cewa suna aiki a kasashen waje yayin da kadan daga ciki suka sauya sana'o'i.

Talauci: Rahoto ya nuna 'yan Najeriya miliyan 27 ke samun kudin shiga N100k a shekara

A wani labarin, wani rahoton Kungiyar Kare Hakkin Bil Adama da Tattalin Arzikin Kasa (SERAP) ya ce ‘yan Najeriya miliyan 27 ne ke samun abin da bai kai Naira 100,000 ba a shekara, inji TheCable.

Kungiyar, a ranar Alhamis 2 ga watan Satumba, ta kaddamar da rahoto mai taken ‘Annobar da aka Manta da Ita: Yadda Cin Hanci da Rashawa a bangaren Lafiya, Ilimi, da Ruwa ke jefa 'yan Najeriya cikin talauci.'

Kara karanta wannan

Cire Tallafi: Kungiyar Ma’aikata Ta Bukaci FG Ta Kara Mafi Karancin Albashi Zuwa N200,000, Ta Yabi Wasu Jihohi

A cewar rahoton, ‘yan Najeriya miliyan 56 na fama da talauci kuma 57.205 daga cikinsu galibinsu na dogaro da kansu ne.

Asali: Legit.ng

Online view pixel