Shugaban kasa ya yi sabon nadi, ya ba Osinbajo sabon aiki, ya nada shugaba a hukumar NCDC

Shugaban kasa ya yi sabon nadi, ya ba Osinbajo sabon aiki, ya nada shugaba a hukumar NCDC

  • Dr. Ifedayo Morayo Adetifa zai hau kujerar Darekta-Janar na hukumar NCDC
  • Sabon Darektan zai canji Dr. Chikwe Ihekweazu wanda zai tafi kungiyar WHO
  • Yemi Osinbajo zai jagoranci kwamitin da zai gyara harkar kiwon lafiya a Jihohi

Abuja - Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nada Dr. Ifedayo Morayo Adetifa a matsayin sabon Darekta Janar na hukumar NCDC ta kasa.

Jaridar Daily Trust ta wallafa rahoto cewa fadar shugaban kasa ta tabbatar da wannan nadin mukami a ranar Litinin, 6 ga watan Satumba, 2021.

NCDC ce hukumar da ta ke yaki da barkewar cututtuka a Najeriya tun bayan da ta samu cin gashin-kai.

Adetifa Morayo Adetifa zai rike NCDC

Kamar yadda shafin LSHTM ya nuna, Dr. Adetifa Morayo Adetifa ya yi digirinsa na farko a jami’ar Ilorin, jihar Kwara a bangaren ilmin likitanci.

Kara karanta wannan

Isa Pantami ya zama Farfesan Jami'a yana rike da kujerar Ministan Gwamnati a Najeriya

Sabon darektan ya kware a harkar ilmin likitancin kananan yara a asibitin koyar da likitoci na jami’ar UNILAG da ke garin Idi-Araba, jihar Legas.

Adetifa ya yi wani digirin a fannin kula da yadda cututtuka suke yadu wa a al’umma. A wannan fanni ya yi digirin PhD a wata jami’ar Amsterdam.

Shugaban kasa
Shugaban kasa Buhari Hoto: @GarShehu
Asali: Facebook

Darektan na NCDC yana aiki ne a makarantar tsabta da ke Landan a kasar Birtaniya, a lokacin da aka ba shi wannan mukami, yana mataimakin Farfesa.

Kafin nan ya yi aiki a kasashen waje, yayi yaki da zazzabin cizon sauro, ya yi bincike a kan tarin tibi.

An ba Osinbajo aiki

Tolu Ogunlesi yace shugaban kasa ya kafa kwamitin da zai gyara sha’ani kiwon lafiya a jihohi da birnin taraya. Yemi Osinbajo ne zai jagoranci kwamitin.

Kara karanta wannan

NCC: Babu maganar dawo da Twitter yanzu duk Najeriya tayi asarar Naira Biliyan 200

Za a zakulo sauran ‘yan kwamitin ne daga masana da malaman kiwon lafiya. Hadimin shugaban kasar yace za a dauko wakilai daga majalisa da gwamnoni.

Ina Chikwe Ihekweazu?

Sabon darektan, Ifedayo Morayo Adetifa zai karbi Chikwe Ihekweazu wanda labari ya zo cewa ya zama matamakin darekta a hukumar lafiya ta Duniya.

A baya an ji shugaban WHO, Tedros Ghebreyesus ya aiko wa Dr. Chikwe Ihekweazu takarda yana sanar da shi zai zama sabon shugaban bada agajin gaggawa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel