Zaben kananan hukumomin Kaduna: PDP ta lallasa APC a akwatin mazabar Gwamna El-Rufa'i

Zaben kananan hukumomin Kaduna: PDP ta lallasa APC a akwatin mazabar Gwamna El-Rufa'i

  • Gwamna El-Rufa'i ya rasa akwatin zabensa ga jam'iyyar PDP a zaben kananan hukumomi
  • Gwamnan ya kada kuri'arsa da safiyar Asabar a akwatin zaben
  • A cewar El-Rufa'i, ba dole bane jam'iyyarsa ta lashe kowani zabe ba

Kaduna - Jam'iyyar Peoples Democratic Party PDP ta lashe akwatin zabe kujerar shugaban karamar hukumar da kuma na kansila a mazabar gwamnan jihar, Nasir El-Rufa'i.

El-Rufa'i ya kada kuri'arsa da safe a akwatin mazabarsa dake Unguwar Sarki, karamar hukumar Kaduna ta Arewa, rahoton ChannelsTV.

Yayinda yake kada kuri'arsa, El-Rufa'i ya bayyana cewa bai zama dole jam'iyyarsa ta APC ta kashe zabe ba, kawai abinda yake bukata shine inganta zabe ta hanyar amfani da na'urar zamani.

A cewar gwamnan, kawo wannan na'urar ua nuna cewa gwamnatin APC a jihar Kaduna ba tada shirin magudin zabe.

Kara karanta wannan

Kano: Dan kwangila ya kai shugaban karamar hukuma kara wurin EFCC kan rike mishi N14.9m

Yayin sanar da sakamakon zaben, baturen zaben mazabar, Muhammad Sani, ya ce jam'iyyar APC ta samu kuri'u 62 a zaben shugaban karamar hukumar, yayinda PDP ta samu kuri'u 86.

A zaben Kansila kuwa, APC ta samu kuri'u 53 yayinda PDP ta samu kuri'u 100.

Yanzu haka, ana cigaba da tattara sakamakon zabe a matattarar zabe na karamar hukumar Kaduna ta kudu.

Zaben kananan hukumomi: PDP ta lallasa APC a akwatin mazabar Gwamna El-Rufa'i
Zaben kananan hukumomin Kaduna: PDP ta lallasa APC a akwatin mazabar Gwamna El-Rufa'i Hoto: channelstv.com
Asali: UGC

An Ɗage Zaɓukan Ƙananan Hukumomi 4 a Jihar Kaduna

Mun kawo muku cewa hukumar zabe mai zaman kanta na Jihar Kaduna, KADSIECOM, ta dage zabukan kananan hukumomi da aka shirya yi a ranar Asabar a kananan hukumomi hudu a jihar saboda rashin tsaro.

Hukumar, a ranar Juma'a, ta ce an dage zabukan ne biyo bayan samun rahoton tsaro wadda ya nuna ba zai yi wu a gudanar da zabukan ba cikin lumana a kananan hukumomin Kajuru, Birnin Gwari, Chikun da Zangon Kataf.

Kara karanta wannan

Da Ɗumi-Ɗumi: An Ɗage Zaɓukan Ƙananan Hukumomi 4 a Jihar Kaduna

Rahoton na Daily Trust ya ce Shugaban hukumar, Dr Saratu Binta Dikko-Audu ya ce dagewar ya zama dole ne domin kare rayyuka da dukiyoyin mutane harda ma'aikatan zaben da kayan aiki.

Asali: Legit.ng

Online view pixel