Amurka ta shirya bada gudumuwa domin tona asirin wadanda ke taimakawa Boko Haram

Amurka ta shirya bada gudumuwa domin tona asirin wadanda ke taimakawa Boko Haram

  • Amurka ta shirya taimaka wa Gwamnatin Tarayya a kan matsalar tsaro
  • Mary Leonard ta ce akwai maganar nemo masu daure wa Boko Haram gindi
  • Jakadar Amurka tace za su taimaka a gano masu taimaka wa ‘Yan ta’addan

Abuja – Punch ta rahoto cewa Kasar Amurka ta bayyana shirinta na tallafa wa Najeriya domin a gano wadanda suke hura wutar ta’addanci a kasar nan.

Jakadar Amurka a Najeriya, Mary Leonard ta bayyana wannan a ranar Litinin, 30 ga watan Agusta, 2021, yayin da ta gana da manema labarai a garin Abuja.

Amurka za ta hada-kai da Najeriya?

An tambayi jakadar ketaren ko gwamnatin Amurka ta shirya bada gudumuwa da nufin a tono wadanda ke daure wa ta’addanci gindin zama a Najeriya.

Mary Beth Leonard mai shekara 59 ta ce yanzu haka ana tattauna wa a game da wannan lamarin.

Kara karanta wannan

Kungiya ta bukaci Gwamnatin Buhari ta binciki bacewar Dadiyata bayan kwanaki 761

“Wannan wani abu ne da muke daukin mu hada kai da Najeriya a kai.”
“Mun yi zama sau uku, muna magana a kan wannan batu a watanni biyu da suka wuce."

Buhari, Joe Biden
Shugaban Najeriya da Joe Biden Hoto: guardian.ng
Asali: UGC

“Ba zan so in shiga bayani dalla-dalla ba.”

Tsoron abin da ya auku a Afghanistan

Jakadar ta kasar wajen a Najeriya ta tabo batun tsoron dangatakar Najeriya da Amurka ya zama kamar yadda lamarin ya kasance a kasar Afghanistan.

A cewarta, akwai alaka mai kyau tsakanin Amurka da Najeriya, wanda hakan ya sa dangantakar da ke tsakaninsu ya sha bam-ban da Afghanistan.

Shugaban dakarun sojojin Amurka a Turai, Janar Jeffrey Harrigian ya bayyana yadda alakar Amurka da Najeriya ta dawo bayan cinikin Super Tucano.

“Cinikin jiragen saman A -29 Super Tucano ya bamu dama mu dawo da alakar da ke tsakaninmu.”

Kara karanta wannan

Kawar dan sanatan da aka kashe ta bayyana abubuwan da suka faru kafin muyuwarsa

A ranar Lahadi ne gwamnatin Jihar Kaduna ta yi karin-haske a kan kisan Kyaftin Abdulkarim Na’Allah, babban 'dan Sanatan Kebbi, Bala Na Allah.

Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya bukaci Jami’an tsaro su gano wadanda ke da hannu a wannan mugun aiki domin a dauki mataki a kansu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel