Yanzu-yanzu: Tsohon sakataren gwamnati, Alhaji Ahmad Joda, ya rasu

Yanzu-yanzu: Tsohon sakataren gwamnati, Alhaji Ahmad Joda, ya rasu

  • Allah ya yiwa tsohon sakataren din-din-din rasuwa
  • Alhaji Ahmad Joda ya yi dogon jinya a asibiti
  • Yan Najeriya da dama sun aika sakon ta'aziyya ga iyalansa

Yola - Tsohon Babban Sakataren Gwamnatin Najeriya lokacin mulkin Soja kuma mutum na farko da Buhari ya ba mukami bayan nasara a 2015 , Alhaji Ahmed Joda, ya mutu.

BBC ta ruwaito daya daga cikin 'yayan marigayin, Asma'u Joda, ta bayyana cewa mahaifinta ya rsu ne yau Juma'a a Yola, babbar birnin jihar Adamawa.

Ya rasu yana da shekara 91 a duniya.

Alhaji Ahmed Joda ya cika ne yana mai shekaru 91 a duniya.

A cewar DT, Ahmad Joda ya rasu ne bayan jinya a asibitin FMC Yola.

Joda ya yi karatunsa a Najeriya da kuma Birtaniya inda ya halarci Kwalejin Pitmans da ke birnin London daga 1954 zuwa 1956.

Kara karanta wannan

Da duminsa: Shugaba Buhari ya dawo gida bayan kimanin makonni biyu a Landan

Ya rike kujeran sakataren din-din-din lokacin gwamnatin mulkin soja ta Janar Yakubu Gowon (Mai murabus).

Yanzu-yanzu: Tsohon sakataren gwamnati, Alhaji Ahmad Joda, ya rasu
Yanzu-yanzu: Tsohon sakataren gwamnati, Alhaji Ahmad Joda, ya rasu

Shugaba Buhari ya dawo gida bayan kimanin makonni biyu a Landan

Shugaba Muhammadu Buhari ya dawo gidan Najeriya bayan zaman ganin Likita na kimanin makonni biyu da yayi a birnin Landan, kasar Birtaniya.

Buhari ya dira a Abuja ne da yammacin Juma'a, 13 ga watan Agusta, 2021.

Mai magana da yawun shugaban kasan, Femi Adesina, ya bayyana hakan da yammacin nan a shafinsa na Facebook.

Asali: Legit.ng

Online view pixel