Karin Bayani: Gwarazan Yan Sanda Sun Ceto Karin Daliban FGC Yauri da Aka Sace

Karin Bayani: Gwarazan Yan Sanda Sun Ceto Karin Daliban FGC Yauri da Aka Sace

  • Wasu ɗalibai guda biyu daga cikin waɗanda aka sace a FGC Yauri, jihar Kebbi sun kubuta daga hannun yan bindiga
  • Rahotanni sun bayyana cewa an gano ɗaliban ne a dajin Ɗansadau dake jihar Zamfara
  • Tun mako shida da suka gabata, wasu yan bindiga suka yi awon gaba da ɗalibai da dama a FGC Birnin Yauri

Yauri, Kebbi:- Wasu ɗalibai biyu daga cikin waɗanda aka sace a makarantar sakandire a jihar Kebbi sun tsero daga sansanin yan bindiga, kamar yadda premium times ta ruwaito.

Ɗaliban biyu, mace da namiji, suna daga cikin gomman da yan bindiga suka sace a sakandiren gwamnatin tarayya (FGC) Yauri, jihar Kebbi.

Rahoton channels tv ya nuna cewa jami'an yan sanda ne suka ceto ɗaliban a dajin Dansadau, ƙaramar hukumar Maru, jihar Zamfara.

Dalibai biyu daga cikin waɗanda aka sace a FGC Birnin Yawuri sun tsero daga hannun yan bindiga
Da Dumi-Duminsa: Wasu Dalibai Daga Cikin Wadanda Aka Sace a Kebbi Sun Gudo Daga Sansanin Yan Bindiga Hoto: punchng.com
Asali: UGC

Kakakin hukumar yan sanda ta jihar Zamfara, SP Muhammed Shehu, ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai a Gusau ranar Lahadi.

Kara karanta wannan

An damke kasurgumin dan bindiga da aka dade ana nema a jihar Sokoto

Yace: "An ceto ɗaliban su biyu suna yawo a dajin yankin Ɗansadau, ƙaramar hukumar Maru a jihar Zamfara."

Shin an biya kuɗin fansa?

Babu wani cikakken bayani ko an biya kuɗin fansa domin kubutar da ɗaliban yayin da ake tantama kan ragowar mutum nawa ne a hannun ɓarayin.

Mako shida da ya gabata ne wasu yan bindiga suka mamaye makarantar FGC Yawuri, inda suka yi awon gaba da ɗalibai da dama tare da malamai huɗu.

A lokacin harin, yan bindigan sun kashe wani jami'an hukumar yan sanda guda ɗaya.

Sace mutane domin neman kuɗin fansa ya zama ruwan dare a jihohin Zamfara, Kebbi da sauran jihohin arewa maso yamma da arewa ta tsakiya.

A wani labarin kuma Gwamnatin Shugaba Buhari Zata Sake Kafa Dokar Kulle Saboda Sabuwar COVID19

Gwamnatin tarayya ta yi gargaɗin cewa Najeriya na gaf da faɗawa matsalar sake ɓarkewar annobar COVID19 a karo na uku a kwanakin nan.

Kara karanta wannan

Babbar Magana: Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba da Daliban Makarantar Sojoji da Dama

Duk da an cigaba da bin dokokin kare yaɗuwar cutar amma an sami mutum 10 da suka harbu da sabon nau'in cutar da ake kira Delta COVID19.

Asali: Legit.ng

Online view pixel