Ba aikin mu bane dakatar da masu fafutuka , sai dai ba za mu laminci rikici ba - Rundunar Sojoji

Ba aikin mu bane dakatar da masu fafutuka , sai dai ba za mu laminci rikici ba - Rundunar Sojoji

  • Sojojin Najeriya suna da kundin tsarin mulki da bai basu damar dakatar da masu fafutuka daga gudanar da zanga-zanga ba
  • CDS General Lucky Irabor ne ya bayyana wannan a yayin wata tattaunawa da tsaffin masu yi wa kasa hidima a Imo a ranar Alhamis, 22 ga watan Yuli
  • Amma duk da haka, Irabor ya ce sojoji ba za su taba yarda da tashin hankali daga duk wanda ayyukansa ke dagula zaman lafiya a kasar ba

Babban hafsan hafsoshin tsaro (CDS) Janar Lucky Irabor ya ce ba aikin sojoji ba ne su dakatar da masu fafutukar siyasa da masu neman ballewa daga shirya kamfen dinsu a Najeriya.

Janar Irabor yayi wannan bayani ne a Imo a ranar Alhamis, 22 ga watan Yuli, yayin tattaunawarsa da hafsoshin kudu maso gabas da suka yi ritaya, jaridar Daily Trust ta rahoto.

Ba aikin mu bane dakatar da masu fafutuka , sai dai ba za mu laminci rikici ba - Rundunar Sojoji
CDS ya bayyana cewa sojoji ba za su lamunci tashin hankali ba a Najeriya Hoto: Audu Marte
Asali: Facebook

Ba za mu lamunci rikici ba

Sai dai kuma, CDS din ya bayyana cewa koda sojoji suna da kundin tsarin mulki da zai hana su yiwa masu fafutukarsu katsalandan a yin taronsu, ba za ta lamunci tashin hankali daga kowa ba a kowani hali, jaridar Vanguard ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Babu wani riba da Buhari ke samu, ba zai yarda da zango na uku ba - Yerima Abdullahi

Ya yi bayanin cewa:

"Ba aikin sojoji ba ne su dakatar da duk wani mai son yin fafutuka. Abu ne na siyasa, amma ba mu yarda da duk wani abu da zai jawo rikici ba kan irin wannan fafutukar.
“Muna da kundin tsarin mulki wanda ya tabbatar mana da hanyoyin da za mu bi domin shawo kan duk wani korafi. Me yasa sai kayi kisan kai kafin ka cimma burin ka?
“Don haka, duk wanda ya saba tanadin kundin tsarin mulki, ba shakka, mu a matsayinmu na hafsoshin soja ko jami’an tsaro ba za mu yarda da hakan ba.”

A wani labari na daban, hare-hare da dama da ‘yan bindiga suka kai a kan al’ummomin Benuwai da Nasarawa sun yi sanadiyyar mutuwar mutane 18 da asarar dukiyoyi.

A ranar Talata, an tattaro cewa kimanin mutane 13 aka kashe lokacin da wasu 'yan bindiga suka kai hari kan wasu garuruwa a yankin Guma da ke Benue.

Kara karanta wannan

Bayan Kame Sunday Igboho, Yarbawa sun magantu kan ra'ayin ballewa daga Najeriya

An kuma rahoto cewa maharan sun kuma auka wa garin na Torkula.

Asali: Legit.ng

Online view pixel