Rikici: Mataimakin gwamna na kokarin karbe kujerar Matawalle, PDP ta yi martani

Rikici: Mataimakin gwamna na kokarin karbe kujerar Matawalle, PDP ta yi martani

  • PDP ta bayyana goyon bayan ta kan cewa, a yanzu, Mahdi Aliyu Gusau shine gwamnan jihar Zamfara
  • A baya gwamnan jihar Zamafa Matawalle ya koma APC, lamarin da ya jawo PDP ta ce kujerarsa dai kam ya rasa ta
  • Biyo bayan hana Gusau shiga ofishinsa a matsayin gwamnan jihar ta Zamfara, PDP ta yi Allah wadai da hakan

An rahoto cewa Mahdi Aliyu Gusau, mataimakin gwamnan jihar Zamfara ya samu goyon bayan jam’iyyar PDP don karbar kujerar Bello Matawalle a matsayin gwamnan jihar dake a arewa maso yamma.

Wannan ya biyo bayan sauya shekar da Gwamna Matawalle ya yi zuwa jam’iyyar APC mai mulki tare da sauran zababbun masu rike da mukaman siyasa a jihar.

Sai dai, Gusau ya tsaya, yana mai cewa ba a zabe shi don ya fice daga PDP zuwa wata jam'iyyar ba, jaridar The Nation ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Ambaliya: Peter Obi Ya Gana da Wani Gwamnan Arewa, Ya Aike da Muhimmin Sako Ga Tinubu, Atiku da Kwankwaso

KARANTA WANNAN: Yadda 'yan gudun hijira suka haifi jarirai sama da 17000 a sansani a jihar Borno

PDP ta shirya karbe kujerar gwamna Matawalle, za ta goyi bayan Mahdi
Mahdi Aliyu Gusau, mataimakin gwamnan jihar Zamfara | Hoto: naijanews.com
Asali: UGC

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Mataimakin gwamnan ya yi hasashen matakin da zai dauka na tsige Matawalle a kan hukuncin Kotun Koli na 2019 wanda ya soke nasarar da dukkan ‘yan takarar APC suka yi a zaben.

Amma, an tattara cewa, rundunar ‘yan sanda ta jihar Zamfara na toshe yunkurin Gusau na karbar mukaminsa na gwamna, lamarin da ya haifar da martani daga PDP a ranar Lahadi, 11 ga watan Yuli.

PDP ta yi Allah wadai da hana Gusau shiga ofis

Da yake magana kan lamarin kakakin PDP Kola Ologbondiyan ya yi Allah wadai da abinda ya kira da yunkurin da 'yan sanda ke yi na gurbata ikon da doka ta ba mataimakin gwamnan.

Kara karanta wannan

Bayan Goyon Bayan Gwamna APC, Sabbin Bayanai Sun Fito Kan Yuwuwar Wike Ya Fice PDP

Jam’iyyar adawar ta yi ikirarin cewa Matawalle ya rasa kujerarsa ne a ranar da ya sauya sheka zuwa APC tare da gargadin ‘yan sanda game da muzgunawa ga mataimakin gwamnan da ake yi.

Ta kuma yi Allah wadai da hukumomin ‘yan sanda a Zamfara kan “haramtacciyar doka da nuna fushin” hana wani taron gangami da mataimakin gwamnan ya shirya.

Jam’iyyar ta PDP ta ce mataimakin gwamnan na da ikon da doka ta ba shi damar hawa kujerar gwamnan “a halin da gwamnan ya bar ofishinsa”, daidai da hukuncin da Kotun Koli ta yanke.

A cewar jam'iyyar, ya kamata 'yan sanda su bai wa mataimakin gwamnan "dukkan kariya da gata" maimakon "muzguna mishi", jaridar The Guardian ma ta ruwaito.

KARANTA WANNAN: Kaduna: Sojoji sun bazama daji don ceto sarkin Kajuru da iyalansa daga 'yan bindiga

Shugabancin Kasa: Yeriman Bakura ya magantu kan tsayawa takara a 2023 karkashin APC

Kara karanta wannan

ISWAP Sun Fara Kafa Sansanoninsu a Yankunan Zamfara, Gwamnatin Jiha ta Koka

A wani labarin, Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Ahmed Yerima, ya ce zai janye takararsa ta kujerar shugaban kasa a 2023 idan har jam'iyyar APC mai mulki ta ba da tikitin zuwa yankin Kudu.

Yerima ya tattara hankalinsa gefe kan babban zaben shekarar 2023 yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja ranar Lahadi, Punch ta ruwaito.

Yerima ya ce bai ga dalilin da zai sa ya fice daga takarar ba, duk da kiran da gwamnonin kudu suka yi a taron su na karshe a Legas.

Asali: Legit.ng

Online view pixel