Yanzu-yanzu: Buhari ya shiga zaman majalisar zartaswa da ministocinsa

Yanzu-yanzu: Buhari ya shiga zaman majalisar zartaswa da ministocinsa

Shugaba Muhammadu Buhari na jagorantar zaman majalisar zartaswa ta yanar gizo karo na 14 a fadar shugaban kasa dake Aso Villa, birnin tarayya Abuja.

An kaddamar da zaman ne misalin karfe 10 na safe inda Buhari ya bukaci aduu'ar Musulmi da Kirista.

Tare da shi a farfajiyar Council Chambers sune mataimakinsa, Farfesa Yemi Osinbajo; Sakataren gwamnatin tarayya, Boos Mustapha; mai bada shawara kan lamuran tsaro, Babagana Munguno; da shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa, Ibrahim Gambari.

Hakazalika akwai Ministoci takwas dake tare da shi a wajen yayinda sauran suka shiga ta yanar gizo.

Ministocin dake wajen sune Rotimi Amaechi (Sufuri); Senator Hadi Sirika (Sufurin jirgin sama); Dr Osagie Ehanire(Kiwon Lafiya); Mrs. Zainab Ahmed(Kudi da kasafin kudi); Abubakar Malami(Antoni Janar); Babatunde Fasola(Ayyuka da jirage); Lai Mohammed(Labarai da al'adu) and Dr Isa Ali Pantami(Sadarwa da tattalin arzikin zamani).

Saurari cikakken labaran...

Yanzu-yanzu: Buhari ya shiga zaman majalisar zartaswa da ministocinsa
Yanzu-yanzu: Buhari ya shiga zaman majalisar zartaswa da ministocinsa
Asali: Twitter

Yanzu-yanzu: Buhari ya shiga zaman majalisar zartaswa da ministocinsa
Yanzu-yanzu: Buhari ya shiga zaman majalisar zartaswa da ministocinsa
Asali: Twitter

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng