Da duminsa: Jihar Flato na kan gaba yayinda Korona ta harbinsabbin mutane 250 a Najeriya

Da duminsa: Jihar Flato na kan gaba yayinda Korona ta harbinsabbin mutane 250 a Najeriya

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 250 a fadin Najeriya.

Kwana hudu a jere yanzu jihar Plateau na zarce Legas da Abuja wajen yawan adadin sabbon wadanda suka kamu da cutar.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:na daren ranar Asabar 29 ga Agustan shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 250 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Plateau-69

FCT-41

Lagos-21

Delta-14

Kaduna-14

Bayelsa-13

Enugu-13

Ekiti-11

Bauchi-9

Ogun-8

Edo-7

Oyo-7

Rivers-6

Adamawa-4

Osun-4

Nasarawa-3

Ebonyi-2

Kwara-2

Gombe-1

Imo-1

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng