Da duminsa: Jihar Flato na kan gaba yayinda Korona ta harbinsabbin mutane 250 a Najeriya
Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 250 a fadin Najeriya.
Kwana hudu a jere yanzu jihar Plateau na zarce Legas da Abuja wajen yawan adadin sabbon wadanda suka kamu da cutar.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:na daren ranar Asabar 29 ga Agustan shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 250 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:
Plateau-69
FCT-41
Lagos-21
Delta-14
Kaduna-14
Bayelsa-13
Enugu-13
Ekiti-11
Bauchi-9
Ogun-8
Edo-7
Oyo-7
Rivers-6
Adamawa-4
Osun-4
Nasarawa-3
Ebonyi-2
Kwara-2
Gombe-1
Imo-1
Asali: Legit.ng