Karin 'yan Najeriya 354 sun kamu da korona, jimilla 45,244

Karin 'yan Najeriya 354 sun kamu da korona, jimilla 45,244

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 354 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:34 na daren ranar Alhamis 6 ga Agustan shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 354 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Karin 'yan Najeriya 354 sun kamu da korona, jimilla 44,890
Karin 'yan Najeriya 354 sun kamu da korona, jimilla 44,890
Asali: Facebook

FCT-78

Lagos-76

Kaduna-23

Ebonyi-19

Oyo-18

Nasarawa-17

DUBA WANNAN: Soja da ta yi ciki bayan ƴan bindiga sun mata fyade ta daukaka kara kan korarta daga aiki

Rivers-17

Delta-16

Kwara-15

Akwa Ibom-13

Edo-12

Ogun-12

Plateau-11

Kano-9

Bauchi-6

Borno-6

Ekiti-6

Alkalluman da hukumar ta dakile cututtukan ta fitar a ranar Alhamis 6 ga watan Agusta shekarar 2020 ya nuna cewa jimillar wadanda suka kamu da cutar ta korona a kasar 45,244 .

An sallami mutum 32,430 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 930.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel