Yanzu-yanzu: An sanar da ranar fara jarabawar NECO da NABTEB

Yanzu-yanzu: An sanar da ranar fara jarabawar NECO da NABTEB

Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa jarabawar kammala karatun sakandare da hukumar jarabar kasa NECO ke shiryawa zai fara ranar 5 ga Oktoba, 2020 kuma a kammala 18 ga Nuwamba, 2020.

Gwamnatin ta kara da cewa hukumar jarabawar NABTEB za ta kaddamar da nata jarabawan ranar 21 ga Satumba kuma a kammala 15 ga Oktoban, 2020.

Karamin ministan ilimi, Emeka Nwajuiba, ya sanar da ranakun jarabawan ne a karshen tattaunawar kwana biyu da yayi da shugabannin hukumomin jarabawar na kasa.

A takardar da kakakin ma'aitakar ilimi, Ben Goong, ya saki, ya ce ma'aikatar ta ce za'a a iya fara jarabawar shiga makarantun sakandaren gwamnatin tarayya ranar 17 ga Oktoba, 2020.

Bugu da kari, jarabawar BECE da daliban aji uku a makarantun sakandare da NECO ke shiryawa zai fara ranar 24 ga Agusta kuma a kammala 7 ga Satumba, 2020.

Yanzu-yanzu: An sanar da ranar fara jarabawar NECO da NABTEB
Yanzu-yanzu: An sanar da ranar fara jarabawar NECO da NABTEB
Asali: Depositphotos

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng