Yanzu-yanzu: Gwamna Fayemi ya kamu da cutar korona

Yanzu-yanzu: Gwamna Fayemi ya kamu da cutar korona

Gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya kamu da cutar korona bayan da ya yi gwajin cutar a karo na uku. Gwamnan ya bayyana hakan ne a wallafar da yayi a shafinsa na Twitter a ranar Laraba.

Kamar yadda ya wallafa, "Na yi gwajin cutar korona a karo na uku a jiya kuma ya bayyana ina dauke da cutar.

"A halin yanzu bana jin wata alamar cutar kuma tuni na killace kaina a gida. Ina samun kulawar likitoci a halin yanzu.

"Na nada mataimakina da ya ci gaba da tafiyar da al'amuran mulki amma zan ci gaba da wasu aiiyukan daga gida."

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng