Yanzu-yanzu: Sabbin Mutane 595 sun kamu da Coronavirus a Najeriya
1 - tsawon mintuna
Hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 595 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:53 na daren ranar Alhamis 16 ga Yulin shekarar 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 595 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:
Lagos-156
Ondo-95
Rivers-53
Abia-43
Oyo-38
Enugu-29
Edo-24
FCT-23
Kaduna-20
Akwa Ibom-17
Anambra-17
Osun-17
Ogun-14
Kano-13
Imo-11
Delta-6
Ekiti-5
Gombe-4
Plateau-4
Cross River-2
Adamawa-1
Bauchi-1
Jigawa-1
Yobe-1
Asali: Legit.ng