Yanzu-yanzu: Sabbin Mutane 595 sun kamu da Coronavirus a Najeriya

Yanzu-yanzu: Sabbin Mutane 595 sun kamu da Coronavirus a Najeriya

Hukumar hana yaduwar cututtuka a Najeriya (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 595 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:53 na daren ranar Alhamis 16 ga Yulin shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 595 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Lagos-156

Ondo-95

Rivers-53

Abia-43

Oyo-38

Enugu-29

Edo-24

FCT-23

Kaduna-20

Akwa Ibom-17

Anambra-17

Osun-17

Ogun-14

Kano-13

Imo-11

Delta-6

Ekiti-5

Gombe-4

Plateau-4

Cross River-2

Adamawa-1

Bauchi-1

Jigawa-1

Yobe-1

Asali: Legit.ng

Online view pixel