Yanzu-yanzu: Sabbin mutane 503 sun kamu da cutar Koronan yau Talata

Yanzu-yanzu: Sabbin mutane 503 sun kamu da cutar Koronan yau Talata

Hukumar Yaki da Yaduwar Cututtuka a Najeriya (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 503 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11.40 na daren ranar Talata 7 ga Yulin shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 503 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Lagos-153

Ondo-76

Edo-54

FCT-41

Enugu-37

Rivers-30

Benue-24

Osun-20

Kaduna-15

Kwara-13

Abia-9

Borno-8

Plateau-6

Taraba-5

Ogun-3

Kano-3

Kebbi-2

Nasarawa-2

Bayelsa-1

Gombe-1

29,879 ne jimmilan wadanda suka kamu

12,108 aka sallama kawo yanzu

669 sun mutu

Asali: Legit.ng

Online view pixel