Yanzu-yanzu: Sabbin mutane 503 sun kamu da cutar Koronan yau Talata

Yanzu-yanzu: Sabbin mutane 503 sun kamu da cutar Koronan yau Talata

Hukumar Yaki da Yaduwar Cututtuka a Najeriya (NCDC) ta ce annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 503 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11.40 na daren ranar Talata 7 ga Yulin shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa karin sabbin mutum 503 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

Lagos-153

Ondo-76

Edo-54

FCT-41

Enugu-37

Rivers-30

Benue-24

Osun-20

Kaduna-15

Kwara-13

Abia-9

Borno-8

Plateau-6

Taraba-5

Ogun-3

Kano-3

Kebbi-2

Nasarawa-2

Bayelsa-1

Gombe-1

29,879 ne jimmilan wadanda suka kamu

12,108 aka sallama kawo yanzu

669 sun mutu

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng