Ba a ga wata ba a Najeriya, Idi sai ranar Lahadi –Sarkin Musulmi

Ba a ga wata ba a Najeriya, Idi sai ranar Lahadi –Sarkin Musulmi

Majalisar Koli ta harkokin addinin musulunci ta Najeriya, NSCIA, ta sanar cewa za a cigaba da azumi a ranar Asabar.

Kwamitin duban wata ta NSCIA ta ce ba a ga wata ba a kasar saboda haka za a cigaba da azumi a ranar Jumaa.

Ta ce za a gudanar da azumi talatin a bana ba kamar yadda wasu musulmi suka fara shirin yin Idi a ranar Asabar ba.

Da ta ke sanar da sakamakon neman watar a ranar Jumaa, ta sanar da cewa "Ba a ga jaririyar watar Shawwal ba a Najeriya, gobe 30 ga watan Ramadan. Za a fitar da sanarwar daga ofishin sarkin musulmi nan ba da dadewa ba."

Ba a ga wata ba a Najeriya, Idi sai ranar Lahadi –Sarkin Musulmi
Ba a ga wata ba a Najeriya, Idi sai ranar Lahadi –Sarkin Musulmi. Hoto daga NSCIA
Asali: UGC

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel