Yanzu-yanzu: Ana artabu tsakanin Soji da yan Boko Haram yanzu haka

Yanzu-yanzu: Ana artabu tsakanin Soji da yan Boko Haram yanzu haka

Dakarun sojin Najeriya dake zaune a Mainok, jihar Borno yanzu haka na artabu da yan kungiyar tada kayar bayan Boko Haram.

TheCable ta ruwaito cewa yan ta'addan sun dira kauyen ne misalin karfe 7 na yamma sun harbin kan mai uwa da wabi.

Majiya yace: "Sun tafi barikin Sojoji kuma na kusan tsawon awa daya yanzu, suna musayar wuta da Sojin,"

A Febrairu, Sojoji bakwai sun rasa rayukansu yayinda yan ta'addan suka kai hari kauyen.

Saurari cikakken rahoton....

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng