Yanzu-yanzu: Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Garba Nadama, ya rasu
1 - tsawon mintuna
Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un Allah ya yiwa Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Garba Nadama, rasuwa.
Ya rigamu gidan gaskiya ne daren Litinin bayan gajeruwar rashin lafiya da yayi fama da shi.
Majiya daga iyalansa sun bayyana cewa nan ba da dadewa ba za'a sanar da lokacin jana'izarsa.
An zabi marigayin ne matsayin mataimakin gwamnan jihar Sokoto a shekarar 1979 kuma ya zama gwamna a watan Nuwamban 1980 bayan rasuwar gwamna Shehu Kangiwa.
Daga baya ya sake takara gwamna a 1093 karkashin jam'iyyar National Party of Nigeria, NPN kuma ya samu nasara.

Asali: Facebook
Asali: Legit.ng