Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 20, Jimilla 343
Cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karin mutane ashirin (20) da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Litinin, 13 ga Afrilu, 2020.
Cibiyar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita inda tace: “An samu karin mutane ashirin (20) sun kamu da #COVID19;
13 a Lagos,
2 a Edo
2 a Kano
2 a Ogun
1 a Ondo
“A karfe 9:30 na daren 13 ga Afrilu, mutane 343 suka kamu da COVID19 a Najeriya. 91 sun warke, kuma 10 sun mutu.“
“An tabbatar da bullar cutar a jihohi 19 a Najeriya.“
Ga jerin jiha-jiha
Lagos- 189 FCT- 56
Osun- 20 Edo- 14
Oyo- 11 Ogun- 9
Bauchi- 6 Kaduna- 6
Akwa Ibom- 5 Katsina-5
Kwara- 4 Ondo- 3
Delta- 3 Kano- 3
Enugu- 2 Ekiti- 2
Rivers-2 Benue- 1
Neja- 1 Anambra- 1
Asali: Legit.ng