Da duminsa: Mutane 10 sun sake kamuwa da Coronavirus a Najeriya

Da duminsa: Mutane 10 sun sake kamuwa da Coronavirus a Najeriya

Cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karin mutane goma (10) da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Lahadi, 5 ga Afrilu, 2020.

Cibiyar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita inda tace: “An tabbatar da mutane goma(10) sun kamu da #COVID19 a Najerya, 8 a Legas, 2 a Abuja, 2 a Edo.“

“Kawo karfe 1:15 na ranar 5 ga Afrilu, mutane 224 aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami mutane 27 , kuma mutane 5 a rigamu gidan gaskiya.“

Da duminsa: Mutane 10 sun sake kamuwa da Coronavirus a Najeriya
Da duminsa: Mutane 10 sun sake kamuwa da Coronavirus a Najeriya
Asali: Facebook

Lagos- 115

Abuja- 45

Osun- 20

Oyo- 9

Akwa Ibom- 5

Ogun- 4

Edo- 9

Kaduna- 4

Bauchi- 6

Enugu- 2

Ekiti- 2

Rivers-1

Benue- 1

Ondo- 1

Asali: Legit.ng

Online view pixel