Da duminsa: Mutane 10 sun sake kamuwa da Coronavirus a Najeriya

Da duminsa: Mutane 10 sun sake kamuwa da Coronavirus a Najeriya

Cibiyar takaita yaduwar cututtuka a Najeriya NCDC ta sanar da cewa an samu karin mutane goma (10) da suka kamu da cutar Coronavirus (#COVID19) a Najeriya a ranar Lahadi, 5 ga Afrilu, 2020.

Cibiyar ta bayyana hakan a shafin ra'ayinta na Tuwita inda tace: “An tabbatar da mutane goma(10) sun kamu da #COVID19 a Najerya, 8 a Legas, 2 a Abuja, 2 a Edo.“

“Kawo karfe 1:15 na ranar 5 ga Afrilu, mutane 224 aka tabbatar sun kamu da COVID19 a Najeriya, an sallami mutane 27 , kuma mutane 5 a rigamu gidan gaskiya.“

Da duminsa: Mutane 10 sun sake kamuwa da Coronavirus a Najeriya
Da duminsa: Mutane 10 sun sake kamuwa da Coronavirus a Najeriya
Asali: Facebook

Lagos- 115

Abuja- 45

Osun- 20

Oyo- 9

Akwa Ibom- 5

Ogun- 4

Edo- 9

Kaduna- 4

Bauchi- 6

Enugu- 2

Ekiti- 2

Rivers-1

Benue- 1

Ondo- 1

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng