Jarumin saurayi dan jihar Nasarawa zai auri mata biyu lokaci daya

Jarumin saurayi dan jihar Nasarawa zai auri mata biyu lokaci daya

Wani jarumin saurayi daga karamar hukumar Keana dake jihar Nasarawa, Ibrahim Kasumi Oboshi, wanda aka fi sani da Ogah ya shirya angwancewa da amarensu biyu a rana daya.

Kasimu zai angwance da Nazira Dahiru Ozegya da Rabi Ishaka Akose wacce akafi sani da Talatu ne ranar 28 ga watan Maris 2020.

Za a gudanar da auren farko ne a karamar hukumar Keana ta jihar Nasaraw misalin karfe 10 na safe sannan a garzaya karamar hukumar Obi domin daura na biyu misalin karfe 12.

Allah ya basu zaman lafiya!!

Jarumin saurayi dan jihar Nasarawa an auri mata biyu lokaci daya
Jarumin saurayi dan jihar Nasarawa an auri mata biyu lokaci daya
Asali: Facebook

Jarumin saurayi dan jihar Nasarawa zai auri mata biyu lokaci daya
Jarumin saurayi dan jihar Nasarawa zai auri mata biyu lokaci daya
Asali: Facebook

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng