Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 5 a Najeriya

Yanzu-yanzu: An samu karin masu cutar Coronavirus 5 a Najeriya

Labarin da ke shigowa da duminsa na nuna cewa an samu karin mutane biyar masu dauke da cutar Coronavirus (COVID-19) a Najeriya, hakan ya kawo adadin yan Najeriya takwas kenan.

Ministn kiwon lafiya, Osagie Ehanire, ya bayyana cewa an samu hudu a Legas, 1 a jihar Ekiti.

Ministan ya kara cewa uku cikinsun sun dawo daga Amurka ne, uwa da diyarta yar mako shida da haihuwa. Sauran biyun kuma daga Ingila suka shigo.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng