Dan Najeriya, Hafiz Idris Abubakar, ya lashe musabakar Al-Qur'ani na duniya
Dan Najeriya, haifaffen jihar Borno, Hafiz Idris Abubakar, ya girgiza duniya inda ya lashe musabakar gasar Al-Qur'ani mai girma ta duniya na Sarki AbdulAziz a birnin Makkah, kasar Saudiyya.
Mahaddatan Al-Qur'ani daga kasashen duniya daban-daban sun yi musharaka a gasar wannan shekara wacce itace karo na 41.
Hafiz Idris Abubakar ya samu kyautan riyal milyan 12 kan wannan gagarumin nasara da yayi.
Kalli hotunan:
Asali: Legit.ng