Bagudu ya mayar da wasu manyan kusoshin gwamnatinsa kan mukamansu
Gwammnan Jihar Kebbi , Abubakar Atiku Bagudu ya tabbatar da sake nadin Dakta Sulaiman Muhammad Argungun a matsayin Shugaban ma'aikatan gidan gwamnati da Alhaji Babale Umar Yauri, Mni a matsayin sakataren gwamnatin Jihar Kebbi karo na biyu.
Nadin su zai fara aiki nan ta ke daga ranar Laraba 5 ga watan Yunin 2019.
Sanarwan nadin na dauke ne cikin wata jawabi da aka fitar a shafin gwamna jihar Kebbi a Twitter.
DUBA WANNAN: Magidanci ya kashe makwabcinsa saboda zarginsa da neman matarsa
Bagudu ya yabawa ma'aikatan biyu bisa hidimar da su ka yiwa jihar tare da shi a mulkinsa zango na farko.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng