Zaben Kano: An fara sakin sakamakon zaben cike-gurbi na Gwamna

Zaben Kano: An fara sakin sakamakon zaben cike-gurbi na Gwamna

Yanzu haka rahotanni na zuwa mana cewa an fara fitar da sakamakon zaben cike-gurbi da aka gudanar a jihar Kano dazu inda aka yi ta samun rikici a wasu mazabun da ake karasa zaben yau a cikin jihar.

Sakamakon da aka fitar ya nuna cewa Abdullahi Umar Ganduje na jam'iyyar APC ne ke kan gaba a zaben inda yake lallasa 'Dan takarar PDP Abba Kabiru Yusuf a mafi yawan kananan hukumomin da aka bayyana sakamakon zaben.

Sakamakon

APC - 45,876

PDP - 10,239

Sababbin sakamakon zabe su na cigaba da fitowa daga Kano:

Karamar hukumar Nasarawa

APC 10,536

PDP 3,409

Karamar hukumar Kibiya

APC 371

PDP 228

Karamar hukumar Dala

APC 2905

PDP 3138

Karamar hukumar Tudun wada

APC 2557

PDP 508

Karamar hukumar Doguwa

APC 1998

PDP 24

Karamar hukumar Albasu

APC 1804

PDP 66

KU KARANTA: Jigon PDP Sanata Kwankwaso ya nemi a sake zabe a Jihar Kano

Karamar hukumar Tofa

APC 628

PDP 190

Karamar hukumar Gaya

APC 1051

PDP 526

Karamar hukumar Bichi

APC: 1,969, PDP: 39

Karamar hukumar Bebeji

APC: 205, PDP: 0;

Karamar hukumar Rogo

APC: 1,033, PDP: 162;

Karamar hukumar Karaye

APC: 1,317, PDP: 27;

Karamar hukumar Rimin Gado

APC: 1,463, PDP: 12;

Karamar hukumar Warawa

APC: 501, PDP: 152

Karamar hukumar Rano

APC: 2,337, PDP: 37;

KU KARANTA: An sake yin ram da wani Kwamishinan Jihar Kano a Ranar zabe

Sauran sakamakon da aka fitar sun hada da:

Karamar hukumar Dambatta

APC: 608, PDP:24;

Karamar hukumar Takai

APC: 4,221, PDP: 149;

Karamar hukumar Albasu

APC: 1,804, PDP: 66;

Karamar hukumar Gabasawa

APC: 728, PDP: 329;

Karamar hukumar Minjibir

APC: 2,414, PDP: 226;

A baya an fitar da sakamakon irin su:

Karamar hukumar Garun Malam

APC - 235

PDP - 01

Karamar hukumar Gezawa

APC= 167

PDP= 27

Karamar hukumar Madobi

APC= 908

PDP= 164

Dawakin Kudu LGA

APC 248

PDP 62

Karamar Hukumar Kibiya

APC - 984

PDP - 05

KU KARANTA: ‘Yan bangar siyasa sun hana mutanen Gama kada kuri’ar su a Kano

Sai dai rahotanni daga Jaridar BBC Hausa sun bayyana cewa an fattataki Ma’aikatan yada labarai na TVC daga cikin Garin Gama inda ake sa rai mutanen kusan 40, 000 za su kada kuri’ar su.

Masu lura da zabe daga wata kungiyar Cleen Foundation sun kuma bayyana cewa babu zaben da yake gudana a irin su Yankin Attawa, Tammawa, Dika, Gulu, Rimin Gado da kuma Jilli da ke cikin Rimin Gado.

Dazu Jaridar Punch ta rahoto cewa Jami’an tsaro sun kuma yi nasarar cafke wani da aka samu da yunkurin sace kayan zabe a akwatin Gama da ke cikin karamar hukumar Hukumar Nasarawa.

A wasu wurare kuma dai ‘yan daba ne su ka zagaye harabar zaben inda su ka hana kowa kada kuri’u. Mu na samun rahotanni cewa ‘yan iskan gari sun dangwale kaf kuri’un wasu Mazabun.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Online view pixel