Rana, Hausawa suka ce bata karya wai sai dai uwar diya taji kunya. Ranar Asabar (yau) dake zaman ranar da hukumar zabe mai zaman kan ta ta kasa ta tsayar kenan domin gudanar da zabukan gwamnoni da 'yan majalisu na raba-gardama na zagaye na biyu.
Akwai jahohi akalla 18 da zabukan za su wakana a yau kamar yadda jadawalin da hukumar zaben ta fitar amma hankulan al'umma yafi karkata a jahohin da za'a gudanar da zabukan na gwamnoni.

Kai-tsaye: Yadda zaben gwamna zagaye na biyu ke gudana a jihar Filato
Source: UGC
Legit.ng ta shirya tsaf domin kawo maku yadda zaben zai kasance a jihar Filato dake Arewa ta tsakiyar Najeriya.
Zaben dai za'a gudanar da shi ne a tsakanin masu neman kujerar gwamnan jihar kuma manya daga cikin su sune na jam'iyyar APC, kuma mai ci a yanzu, Mista Simon Lalong da kuma na jam'iyyar adawa ta PDP, Mista Janar Useni.
Dan takarar jam'iyyar APC ne ke kan gaba dai a zaben farko da aka gudanar.
An soma kada kuri'a a wata mazaba a karamar hukumar Barikin Ladi
Zabe na gudana a karamar hukumar Jos cikin gari
A karamar hukumar Mangu ma zabe na tafiya lafiya lau
Sakamakon zabukan rumfuna sun soma kammaluwa a wasu sassa na jihar Filato
Ga wani sakamakon nan ma:
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com