An haifi jaririya dauke da rubutun sunan Allah a Sokoto
Rahotanni da ke zuwa mana yayi ikirarin cewa an haifi wata jaririya dauke da rubutun sunan Allah a wasu bangarori na jikinta ciki harda kirjinta. Anyi zargin cewa yarinyar na dauke da rubutune a jirginta, jinta da kuma bayanta.
An tattaro cewa an haifi jinjirar ne a ranar 2 ga watan Maris, sannan kuma haihuwarta ya janyo hankulan mazauna Sokoto da dama wadanda ke tururuwan zuwa ganin abunda mahaifiyar yarinyar, Saratu Yusuf ta bayyana a matsayin baiwa daga Allah.
Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa an haifi yarinyar a cikin iyalai hudu. An kuma haife ta ne a asibitin yan sanda da ke hanyar Barth Sokoto, mahaifiyar yarinyar ta bayyana cewa ta haifeta kamar kowa sannan cewa ba ta fuskanci wani bakon lamari ba a lokacin da take dauke da cikin yarinyar.
Saratu wacce ta haifi jinjirar tare da mijinta na shekara 16, Alhaji Hussaini, ta bayyana cewa ta lura da yadda fatar jikin yarinyar yaki huduwa. Ta bayyana cewa a lokacin da suka yi kokarin huda mata kunne, ba abunda ya shia jikinta.
KU KARANTA KUMA: Zaben Nasarawa: Dan takarar gwamna a PDP ya ki amincewa da sakamakon zabe, ya doshi kotu
Da take nuna farin cikinta, mahaifiyar yarinyar ta bayyana cewa abun farin ciki ne samun irin wannan baiwar a gidanta. Ta kuma bayyana cewa yarinyar ta janyo hankulan baki daga kananan hukumomi daban-daban na Sokoto sannan cewa ta koma wani wuri mai shiru saboda hayaniya.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng