Da duminsa: Rundunar sojin Najeriya na artabu da yan Boko Haram a MalamFatori - Ahmed Salika

Da duminsa: Rundunar sojin Najeriya na artabu da yan Boko Haram a MalamFatori - Ahmed Salika

Rahoton da ke shigo mana na nuna cewa rundunar sojin Najeriya dake jihar Borno suna musayan wuta da yan kungiyar tada kayar bayan ISWAP da suka balle daga cikin Boko Haram a garn Malam Fatori, jihar Borno.

Legit Hausa ta samu wannan rahoto ne daga dan jaridan nan da ya shahara da ruwaito labarun Boko Haram, Ahmad Salkida.

Ya bayyana hakan ne a shafin ra'ayi da sada zumuntarsa na Tuwita da yammacin Litinin, 3 ga watan Disamba, 2018. Yace: "Rundunar sojin Najeriya na cikin artabu da mayakan ISWAP a Malumfatori."

Zamu kawo muku cikakken rahoton....

Asali: Legit.ng

Online view pixel