Hadimin matar gwamnan Bauchi ya kwanta dama

Hadimin matar gwamnan Bauchi ya kwanta dama

Alhaji Bello Galadima, Hadimin uwargidan gwamnan jihar Bauchi, Hajiya Hadiza Mohammed Abubakar ya rasu.

Labaran rasuwarsa yana dauke cikin wata sanarwa ne da ta fito daga, Rashida Yusuf sakataren yadda labarai na uwargidan gwamnan.

Uwargidan gwamnan ta yi juyayin rasuwarsa inda ta bayyana cewar mutum ne mai aiki tukuru kuma ya gudanar da ayyukansa iya kokarinsa a lokacin da ya ke raye.

Hadimin matar gwamnan Bauchi ya kwanta dama
Hadimin matar gwamnan Bauchi ya kwanta dama
Asali: Facebook

Hajiya Abubakar tayi addu'ar Allah ya jikansa, ya yafe kurakurensa ya kuma saka masa da gidan aljanna.

DUBA WANNAN: Gwamnatin tarayya ta fitar da daftarin kasafin kudin shekarar 2019

Ta bukaci iyalan mammacin su dauki rasuwarsa a matsayin kaddara daga Allah kuma tayi addu'ar Allah ya basu hakurin jure rashinsa.

Kafin rasuwarsa, marigayi Bello Galadima shine mataimakin na musamman kan tsare-tsare da hidimomi na Hajiya Hadiza Mohammed Abubakar.

A wata rahoton, Legit.ng ta kawo muku cewa kotun tarayya da ke Abuja ta bawa tsohon gwamna jihar Adamawa, Murtala Nyako izinin fita kasar Jamus domin likitoci su duba lafiyarsa.

Hukumar EFCC ne ta gurfanar da Nyako da yaransa bisa zarginsa da karkatar da kudin al'umma yayin da ya ke gwamna a jihar.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta NAIJ.com Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164