Takarar Sanata: Makarfi ya kunyata jam'iyyar PDP, ya ce akai kasuwa
- Makarfi ya kunyata jam'iyyar PDP, ya ce akai kasuwa
- Yace shi bai da ra'ayin yin takarar Sanata
Daya daga cikin wadanda suka yi takarar tikitin takarar shugaban kasa a jam'iyyar PDP Sanata Ahmed Mohammed Makarfi ya karyata rade-raden cewa an bashi tikitin takarar Sanata a jam'iyyar a zaben 2019 biyo bayan rashin nasarar da yayi a zaben fitar da gwani.

Asali: Twitter
KU KARANTA: Bafarawa na shirin barin PDP ne?
Shi dai Makarfi ya yi takarar tikitin shugaban kasa ne tare da wasu mutane 11 a jam'iyyar ta PDP amma bai samu nasara ba inda tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya lashe zaben da gagarumin rinjaye.
To sai dai wasu rahotannin da sukayi ta yawo sune na cewa jam'iyyar ta PDP ta baiwa dukkan wanda yayi takarar shugaban kasar amma bai samu nasara ba tikitin takarar Sanata kai tsaye tun kafin zaben.
A wani labarin kuma, Gwamnan jihar Ekiti dake a yankin Kudu maso yammacin kasar nan mai barin gado, Ayodele Fayose ya tattara yanasa-yanasa ya fice daga jihar biyo bayan hannun ta takardun barin gwamnati da yayi a ranar Juma'ar da ta gabata.
Gwamnan dai ya bar jihar ne da yammacin ranar Lahadi jim kadan bayan kammala wata ibada ta musamman da yayi a cocin gidan gwamnatin jihar wadda ta samu halartar manya a ciki da wajen jihar.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa
Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng