Dandalin Kannywood: Ku duba sabbin kyawawan hotunan Nafisa Abdullahi da kowa ke magana

Dandalin Kannywood: Ku duba sabbin kyawawan hotunan Nafisa Abdullahi da kowa ke magana

Yayin da wasu ke kiran jaruma Nafisa Abdullahi da suna sarauniyar kyau a farbajiyar masana'antar shirya fina-finan Hausa, wasu kuwa kiran ta suke yi da macen dawisu uwar ado watakila saboda yadda ta iya caba kwalliya.

Koma dai menene, tabbas jarumar tana daya daga cikin fitattun jarumai mata a masana'antar shirya fina-finai ta Kannywood da za'a sa a cikin jerin kyawawa da kuma suka bayar da gudummuwar su sosai wajen cigaban masana'antar.

Dandalin Kannywood: Ku duba sabbin kyawawan hotunan Nafisa Abdullahi da kowa ke magana
Dandalin Kannywood: Ku duba sabbin kyawawan hotunan Nafisa Abdullahi da kowa ke magana

KU KARANTA: Yan kwankwasiyya sama da dubu 500 sun koma PDP a Edo

Legit.ng ta yi kicibis da wasu hotuna da jarumar ta saka a shafin ta na dandalin sadarwar zamani cikin shiga irin ta kamala tare da rufe jikin ta ruf sanye da riga mai rodi-rodinkayan sojoji.

Al'umma da dama dai ma'abota anfani da kafar sadarwar da suka hada da masoya da ma akasin haka duk sun yabawa jarumar musamman ma irin shigar da tayi ta kamala sabanin irin yadda jaruman suka saba.

Haka zalika jarumar ta sha yabo tare da addu'o'i daga jama'a a saboda hakan inda suka yi kwarara mata addu'ar karin daukaka cike da rayuwa mai albarka.

Ga dai karin wasu hotunan nan:

Dandalin Kannywood: Ku duba sabbin kyawawan hotunan Nafisa Abdullahi da kowa ke magana
Dandalin Kannywood: Ku duba sabbin kyawawan hotunan Nafisa Abdullahi da kowa ke magana

Dandalin Kannywood: Ku duba sabbin kyawawan hotunan Nafisa Abdullahi da kowa ke magana
Dandalin Kannywood: Ku duba sabbin kyawawan hotunan Nafisa Abdullahi da kowa ke magana

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel