Yanzu Yanzu: Kotu ta dakatar da tsige Gwamnan jihar Benue, Ortom

Yanzu Yanzu: Kotu ta dakatar da tsige Gwamnan jihar Benue, Ortom

Wata babbar kotun Makurdi karkashin jagorancin Justis Theresa Ogoche, ta dakatar da dakatattun mambobin majalisar dokokin jihar Benue daga kokarin tsige gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom.

Mai shari’an ta kuma dakatar da su daga zama sannan ta goyi bayan dakatar dasu zuwa lokacin da za’a fadi makomar lamarin.

Yanzu Yanzu: Kotu ta dakatar da tsige Gwamnan jihar Benue, Ortom
Yanzu Yanzu: Kotu ta dakatar da tsige Gwamnan jihar Benue, Ortom

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Kotu ta bayar da umurnin kama shugaban INEC, Mahmoud

Justis Igoche ta goyi bayan umurnin da Justis Adam Onum, babban alkalin jiha ya yanke a baya na hana tsohon kakakin majalisar, Terkimbi Ikyange, da sauran manyan jami’ai daga sintiri kan haka sannan kuma ta umurci hukumomin tsaro da su bar harabar majalisar dokokin jhar Benue.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel