Boko Haram sun dawo tare tituna, sun kar mutane daren jiya a hanyar Dikwa

Boko Haram sun dawo tare tituna, sun kar mutane daren jiya a hanyar Dikwa

Ana fargabar cewa mutane da dama sun rasa rayyukansu sakamakon harin da 'yan ta'addan Boko Haram suka kai yayin da suka tare matafiya a babban titin Borno a ranar Talata.

Daily Trust ta ruwaito cewa 'yan ta'addan sun tare matafiyan ne a tsakanin Ramin Aljanu da Logumani da hanyar kauyen Musane dake babban titin zuwa Dikwa/Ngala.

Sun kashe fasinjoji da dama bayan sun tare su. Sun kuma kona motoccin dake dauke da fasinjojin.

Boko Haram sun dawo tare tituna, sun kar mutane daren jiya a hanyar Dikwa
Boko Haram sun dawo tare tituna, sun kar mutane daren jiya a hanyar Dikwa

A wata rahoton, Legit.ng ta kawo muku yadda 'yan bindiga suka kai hari wasu kauyukka a jihar Zamfara inda suka hallaka mutane sama da 30.

Ku biyo mu don samun karin bayani ...

Asali: Legit.ng

Online view pixel