Badakalar naira biliyan N5.3bn: Kotu ta ba da umarnin kama tsohon gwamnan Enugu Ken Nnamani
- Kotu ta bada umarni kama Ken Nnamani akan almundahana da naira biliyan N5.3bn
- Jastis Chuka Obiozor ya bada umarnin kama tsohon gwamnan saboda yaki halarta kotu a ranar Litinin
- Lauyan Ken Nnamani ya kasa kare maigidan sa kotu akan kin gabatar da kansa a gaban alkali
Wata Babbar kotu tarrayya dake jihar Legas ta ba da umarnin kama tsohon gwamnan jihar Enugu, Chimaroke Nnamani, bisa zargin sace naira biliyan N5.3bn.
Jastis Chuka Obiozor ya bada umarnin kama tsohon gwamnan saboda yaki halarta kotu a ranar Litinin bayan an ba shi takardar gayyata.

Lauyan Ken Nnamani ya kasa kare maigidan sa kotu akan kin zuwa kotu bayan an gayyaci shi.
KU KARANTA : Hukumar JAMB ta sanar da ranar da za ta fara sayar da fom din jarabawa
Ken Nnamani na daga cikin tsofaffin gwamnonin Najeriya da kotu ta ba da umarinin tsare su bisa zargin almundahana da kudaden jihohin su a cikin wannan shekara.
Latsa Wannan: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa
Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng